Friday, December 20, 2013

Kano ta sake aurar da wani rukunin zawarawa...






https://blogger.googleusercontent.com/img/b/R29vZ2xl/AVvXsEiRjUGAyMuej9VTnWTwIqyRu00_mOKqxeNlcICspJ6Pm1BvwRDbRL-C7qBtvxhZezRQROEOxEhApECAO6jLv_7jxp2IlJvtpj0uH8cgUql3pgaKmVNJF57RlhMNv1FfXgle0YNjqyg5-Sgd/s1600/1.jpg
Jerin wasu amare da angwaye


A jiya  ne gwamnatin Kano ta sake aurar da wasu rukunin zawarawa har da 'yanmata karo na hudu, inda ta aurar da dubu daya da dari daya da goma sha daya, sittin daga ciki mabiya addinin kirista ne.

Kamar yadda al'adar shirin yake an bai wa kowacce amarya tagomashin dubu ashirin lakadan amatsayin jari sa'annan kamfanin yahuza suya ya gwangwaje kowacce amarya da kullin murgujejiyar kaza.


Rahotanni sun bayyana cewa an akashe akalla Naira miliyan dari biyu da saba'in da takwas wajen bikin auren.


Kayan dakin da aka baiwa kowacce amarya

No comments:

Post a Comment