Tuesday, December 17, 2013

Daliban Jami'a ina kuke?



Daliban jami'a

A jiya ne kungiyar malaman jami'a na ASUU suka janye yajin aikin tsawon wata  biyar, kungiyar ta janye yajin aikin ne bayan da aka cimma matsaya tsakaninta da gwamnatin tarayya, wanda shugaban kungiyar kwadago Comrade Abdulwaheed Omar ya wakilci gwamnatin tarayyar...an yi zaman sulhun ne a jami'ar fasaha na garin minnan jihar Neja.

Dan haka daliban jami'a sai  a tattara komatsai a koma makaranta...haka Allah yaso da ku, ku da baku da gatan karatu a kasashen waje!!

No comments:

Post a Comment