Wednesday, October 29, 2014

Gwamna Kwankwaso ya kaddamar da aniyarsa ta neman tsayawa takarar shugabancin kasarnan.

Gwamna Rabiu Musa Kwankwaso
A jiya ne Gwamnan jihar Kano Dr.Rabiu Musa Kwankwaso ya kaddamar da aniyarsa ta neman tsayawa takarar shugabancin kasarnan a karkashin Inuwar babbar jam'iyar Hammaya ta APC.

Kwankwaso wanda ya yi bikin kaddamawar a babban birnin tarayya Abuja,ya shaida cewa ya samu nasarori da dama da suka zame masa tsani na zama shugaban Kasa a Nijeriya.

Gwamna Kwankwaso ya ce zai amince da yin sulhu tsakanin wadanda suke neman takarar shugabancin Kasarnan a APC, muddin aka bayyana masa sharuddan daya sa za a nemi ya janye takarar tasa.

Tuni dai tsohom mataimakin shugaban kasarnan Atiku Abubakar da Tsohon shugaban kasa Janar Muhammad Buhari mai riyata suka ayyana sha'awar tsayawa takarar shugabancin kasarnan a inuwar jam'iyar ta APC.

A watan gobe ne dai babbar jam'iyar hamayya zata yi zaben fidda gwani, domin tsaida mutum gudada zai tsaya mata takarar shugabancin kasarnan a zaben shekara 2015