Monday, November 18, 2013

Kwankwaso ya lashe kyautar zakaran gwamnoni ta bana.

Photo
Gwamna kwankwaso na karbar lambar yabo











Bikin Fina-finai na Afrika da aka gudanar a kasar Ingila ya karrama gwamnan jihar Kano Dr Rabi'u Musa Kwankwso saboda rawar da ya  ke takawa wajen inganta harkar ilimi da tallafawa  
   matasa. Yayin da  takwaransa na jihar Sakkwato Aliyu Wamako ya lashe kyautar zakaran gwamnoni a kan aiyukan raya kasa. 

Kwankwason ya bayyanawa manema labarai cewa wannan kyauta za ta kara masa karsashi wajen bunkasa ci gaban  matasa, gwamnan ya kuma yaba da hazaka ga daliban da suke karatu a can kasar ta Ingila.

Hausawa dai kan ce mai kamar zuwa kan aika!!!


No comments:

Post a Comment