Monday, February 3, 2014

Mawakiya Fa'iza Badawa


Mawakiya Faiza Badawa
Ga wadan da basu san ta ba su ke jin wakokin ta,to yau zauren mu ya yi katarin ganawa da ita ga kuma tsarabarta a takaice:

An haifi matashiyar  mawakiya Fa'iza  a unguwar 'Yankaba a cikin birnin Kano Shekaru 23 da suka gabata.

Ta fara waka a shekara 2004 da wakokin yabo, wacce wakar Isra'i ta kasance ta farko..Daga cikin wakokin yabon akwai Kano ta Manzon Allah, Buri na zuciya , Ya rasulillahi, Agaji da sauransu.

Haka kuma mawakiyar ta kuma yi fice a wakokin fina-finan Hausa na Kannywood inda tace bata ma san adadin su ba, daga cikin wakokin fim din Kannywood akwai Daren alkhairi, Babbar rabo, Babban yayana, Tunziri, Zaman idda da sauransu.

 Haka kuma mawakiyar ita ce ta rere wakar Radiyo wazobia a kano ba a samu kamar ki ba... 

No comments:

Post a Comment