Friday, September 5, 2014

Za a bude makarantu aranar 22 ga watan Satumba



'Yan makaranta

 A yau ne gwamnatin tarayya ta bada umarnin  a bude makarantun firamare da na sakandire a ranar Litinin 22 ga watan Satumbar da muke ciki.

Hakan ya biyo bayan ganawar da aka yi tsakanin Ministan ilimi Mal. Ibrahim Shekarau da kwamishinonin ilimi na jihohin Kasarnan.

Idan za a iya tunawa an dage komawar makarantun zuwa 13 ga watan Oktoba saboda daukar matakai wajen dakile yaduwar cutar Ebola.

No comments:

Post a Comment