Tuesday, September 9, 2014

Maniyata daga Kano za su fara tashi a yau

Kasa mai tsarki
 Kimanin maniyata dari biyar da hamsin ne zasu fara tashi zuwa kasa mai tsarki daga nan jihar Kano.
Jami'in hulda da jama'a na hukumar alhazai ta jihar Alhaji Sani Tanko ya shaida hakan ga manema labarai.

Alhaji Tanko yace maniyatan sun fito ne daga kananan hukumomin Wudil, Warawa, Ajingi, Takai, Albasu da kuma Gaya, wadanda za su tashita jirgin kamfanin Max Air.

Jami'in ya kara da cewa daga cikin jiragen da za su yi jigilar maniyatan sun hada da Max Air, Sky Power da kuma jirgin Kabo.

A cewar Tankon, an jawo lokacin fara jigilar alhazan ne daga Laraba zuwa yau Talata sakamakon kammala shirin fara jigilar da kamfanin Max Air ya yi ,inda alhazan za su tashi da karfe goma na daren yau.

No comments:

Post a Comment