Friday, August 15, 2014

Likitoci masu neman kwarewa sun yi zanga-zanga


Likitoci masu neman kwarewa sun yi zanga-zanga domin nuna rashin gamsuwarsu bisa matakin da gwamnatin tarayya ta dauka na korar likitoci kusan dubu goma sha shida a kasarnan.

Likitocin wadanda suka gudanar da zanga-zanga akarkashin kungiyarsu, sun bayyana takaicinsu ga uwar kungiyar likitoci ta kasa a birnin Abuja.

Shugaban kungiyar likitocin masu neman kwarewa Jibril Abdullahi ya yi Allah wadai da matakin da gwamnatin ta dauka na soke koyarda aikin kwarewa akanaikin likita akasarnan.

Da yake karfafa musu gwiwa shugaban kungiyar likitoci ta kasa(NMA)Dr. Kayode Obembe ya bukaci gwamnatin tarayya da ta gaggauta janye kalamanta nadakatar da likitocin.

Masu zanga-zangar daisuna dauke da kwalaye dauke da kalamai daban-daban

No comments:

Post a Comment