Friday, August 15, 2014

Dangote ya bada gudummawar Naira Miliyan 150 domin yaki da cutar Ebola


Aliko Dangote

Attajirin nan Alhaji Aliko Dangote ya bada gudummawar Naira Miliyan 150 domin taimakawa wajen yaki da yaduwar cutar Ebola a Najeriya.

Shugaban gidauniyar Dangote Mrs Ahiambo Odaga ta bada sanarwar a wani zama da akayi da Ministan Lafiya a babban birnin tarayya Abuja.

Madam Odaga ta bayyana cewa Alhaji Aliko Dangote ya yi kira ga ' yan Najeriya da su bada goyon baya  ga  Gwamnatin Tarayya wajen yaki da cutar Ebola inda ya bayyana fatansa na magance Cutar.

No comments:

Post a Comment