Friday, May 30, 2014

Saima Muhammad ta zama Amarya!!



Jaruma Saima da Angonta
A gobe Asarbar ne 31 ga watan Mayun shekara 2014 za a daura auren Jarumar kannywood Saima Muhammad ,A unguwar Gama, Brigade cikin birnin Kano da  Misalin Karfe sha daya  na safe.

Idan ba a manta ba Saima na daga cikin  jaruman sahun farko na  Kannywood,daga cikin fina-finan ta akwai Kilu ta ja bau wanda shi ne fim dinta na farko da aka yi a shekara 1996 zuwa 1997 da Kamfani Iyantama Multimedia suka shirya,sai  Iyaka, 'Yanmata,Mumbari, Khushu'i da Zuri'a da sauran makamatansu.

Ko kun san cewa fim din kilu ta ja bau shi ne  fim din da ya fara jan hankalin 'yan mata da samari shiga harkar fim? Saima ta fito da sunan Aina'u a fim din,Kuma fim din ya yi kasuwa...

Muna yi mata fatan alheri...

No comments:

Post a Comment