Monday, May 5, 2014

Allah sarki...Akwana a tashi...

Marigayi Umaru Musa Yar'adua

A rana irin ta yau 5 ga watan Mayu shekara 2010 shugaban kasa Umaru Musa Yar'adua ya kwanta dama sakamakon rashin lafiya da ya sha fama.

Kafin rasuwarsa,shi ne shugaban kasar Najeriya  na 13,Ya kuma rike mukamin gwamnan jihar Katsina daga  29 ga watan Mayu shekara 1999 zuwa 29 ga watan Mayu shekara 2007.

Shi ne ya lashe zaben Shugaban kasa mai cike- da kace-nace karkashin Jam'iyar PDP da aka gudanar a 21 ga watan Afrilu kuma aka rantsar da shi a ranar 29 ga watan Mayu shekara 2007
.
A Shekara 2009 Ya bar gida Najeriya zuwa Kasar Saudiya domin duba lafiyarsa abisa matsalar da ta shafi Koda.
A ranar 24 ga watan Fabrairu 2010 ya dawo gida Najeriya bayan ya sha fama da jinya ,inda ya rasu a ranar 5 ga watan Mayu,A ka kuma binne shi aranar 6 ga watan Mayu  a Unguwar Yar'adua.
Ya rasu ya bar Mata daya da 'ya'ya takwas...

 Yau shekaru hudu kenan da ya bar duniya...Allah ya jikansa ya gafarta masa... 

No comments:

Post a Comment