Friday, September 20, 2013

Sabuwar jam'iyar PDP ta zargi fadar shugaban kasa da makarkashiyar sauya shugabanci a majalisar dokokin Najeriya.

majalisar dokoki
majalisar wakilai

           



majalisar dattijai
  


Sabuwar jam'iyar PDP ta zargi fadar shugaban kasar Najeriya da yin makarkashiyar tsige shugaban majalisar dattijai David Mark da takwaransa kakakin majalisar wakilai Aminu Tambuwal.

Sai dai fadar gwamnatin ta musanta zargin inda ta danganta zargin amatsayin yarfe ne na 'yan adawa.

Zargin ya biyo bayan wani yunkurin kafa kingiya da tsagin masu yiwa Bamanga Tukur biyayya suka kafa domin sanyawa kakakin ido da niyyar zakulo aibinsa.

A nasa bangaren sakataren sabuwar jam'iyyar PDP Chukwuemeka Eze ya gargadi masu shirin kulla wannan makirci su sake tunani.
Hausawa dai kan ce "Idan za ka gina ramin mugunta gina shi gajere".....

No comments:

Post a Comment