Thursday, September 19, 2013

Dangote kai kadai gayya....



 
  Alh.Aliko Dangote


Kama ta ya yi batun yadda rukunin kamfanonin Dangote ya kammala shirye-shirye domin kafa harsashin gina matatar mai mafi girma a nahiyar Afrika, ta sanya 'yan Najeriya tsalle da dokin cewa a karshe kasarsu ta kubuta daga kwamacalar da ta tsince kanta aciki ta kuma kama tafarkin kai wa ga matsiyinta na giwar Africa.

Matsalar karacin man fetir, matsala ce da ta dade ta na ciwa shuwagabanin siyasar Nijeriya tuwo a kwarya da kuma har yanzu suke kasa warware ta, duk da kasancewar kasa a sahun gaba wajen samar da
danyen man fetir.

Wanna shafin, zai bayyana muku yadda wannan sanarwa ta zama wani abin alfahari a tsakanin 'yan Nijeriya tun bayan da kasar ta gano manfetur, domin kuwa kafa katafariya matatar mai zai kasance wani al'amari da ya dara samun man alheri.
Anan muna iya cewa Dangote zai jefi tsuntsu biyu da dutse daya.

Matsalar wutar lantarki, ita ce kan gaba wajen dakile kokarin 'yan Nijeriya na samun cigaba, kasancewar gwannati ta gaza a wannan fanni. To kaga anan, idan manfetir ya wadatu, 'yan Nijeriya zasu sarrafa shi wajen samar da wutar lantarkin. Wanda hakan kadai ma ya isa ya 'yanta dimbin basirar sana'oi da Allah ya albarkaci matasan Nijeriya da shi.

Kuma hakan zai rage yawan gurbatar iska da hayakin da dan karamin janaetan nan da 'yan Najeriya ke yiwa lakani da "I pass my neighbour" (na dara makwabci na).
Hakan zai kawo mashahurin sauyi ta yadda 'yan Nijeriya da suka yi gudun hijira zuwa makwabtan kasashe domin yin sana'oi zasu dawo gida.
.
Alfanun da kafa wannan matatar mai zai samar sun hada da : Dakile matsalar almundahana, idan aka tuna  da yadda aka yi amfani da batun tallafin manfetir wajen wawure kudaden 'yan Najeriya da rana tsaka. To ka ga anan, idan matatar nan ta fara aiki,zata rufe kafar bukatar siyo tataccen mai daga kasashenketare,ka ga batun tallafin shigo da tataccen mai ya kau.

Kamfanin Dangote ya sha samun nasarori, duba ga  cewa kamfanin simintin sa,na daya daga cikin aiyukanda aka fara,aka kuma kammala akan lokaci. Kuma a iya  kudin da aka iyakance wajen kammala su.
Akwai abin ban mamaki yadda shuwagabannin Najeriya suka kasa warware matsalolin kasar duk da cewa yawankudin da suke da shi ya dama na Dangote, ammairin nasarorin da ya samu babu wani dan siyasar da zai bugi kirji ya ja da shi.

Galibin mutane sun zaci da injinan janareta ake samar da lantarkin da ake gudanar da manyan masana'antu a kasashen da suka cigaba,kasancewar a Najeriya. Injin janareta shi ne babbar hanyar samar da wutar lantarki ga kowa, har ma da masu hannu da shunin da suka mallaki jiragen kawunansu.
Shin wannan bai zama tamkar tupka da warwara ba?

Abin mamaki ana shi ne gazawar wadannan shugabannin siyasa ya gaza tadiye irin nasarorin da Dangoten ya samu, yadda gwamnatoci suka gaza wajen samar da wutar lantarki amma shi ya samar da ita da rukunin kamfanoninsa ya samu.

A ra'ayi na,abin da 'yan Najeriya ke bukata shi ne a samu karin irin su Dangote, ba wai 'yan siyasa ba. Dan haka duk sa'ilin da 'yan Najeriya suka yi addu'a kamata ya yi su roki karin masu zuciya irin su Dangote ba wai mayaudaran 'yan siyasa ba.

Akalla dai ace an samu wanda ya samar da wutar lantarki,duk da cewa dai ta takaita ga rukunin kamfanoninsa.
Hausawa dai na cewa "girma ya fadi da Rakumi ya shanye ruwan 'yan tsaki"

No comments:

Post a Comment